Would you like to receive notifications on latest updates of the following headlines?

Cikar Kwanaki 100 A Offis: Zulum Ya Gabatar Da Sakamako 77

POSTED ON September 11, 2023 •   HAUSA      BY Hauwa Aliyu Balasa
Gwamnatin jihar Borno ta ce ta aiwatar da ayyuka 77, wannan na zuwa ne gab da shirye-shirye nuna wasu muhimman ayyuka a cikin kwanaki 100 a ofis da gwamnar jihar yayi. Bugu da kari kuma  wannan shine karo na biyu da Gwamna Zullun yake kan karagar mulkin jihar,Sakataren gwamnatin jihar, Bukar Tijjani, ya fitar da katin makin na kwanaki 100 a kan karagar mulki ranar Litinin a Maiduguri. A cewarsa, Zulum ya gudanar da ayyuka 10 a fannin ilimi wadanda suka hada da makarantun Mega uku, daukar malamai 4,000, gina gidajen malamai 30 da kuma biyan kudin tallafin karatu ga dalibai 14,284 a Najeriya da wasu 30 da ke karatu a kasashen waje. A fannin kiwon lafiya, sakataren gwamnatin jihar ya ce an samar da ayyuka biyar, wadanda suka hada da gina cibiyoyin kiwon lafiya guda hudu tare da kowannensu yana da karfin gadaje 30 da wuraren jinya. “Wadannan cibiyoyin kiwon lafiya su ne na matakin farko,a Limankara da ke Gwoza, Kaleri a Mafa, Zarmari a Konduga da Shuwari II a MMC, su ne wanda mataimakin shugaban kasa Kashim Shettima ya kaddamar a ranar Juma’a. Tijjani ya kuma yi bayani kan fitar da Naira biliyan 2 domin biyan basussuka ga ma’aikatan gwamnati kuma an rubanya kudaden gratuti a duk shekara zuwa Naira biliyan 2.4 don magance koma bayan kudaden gratuti da ake bin ma’aikatan da suka yi ritaya. An kuma fitar da Naira Biliyan 1 a matsayin karin tallafi ga wadanda bala'in gobara a kasuwar Maiduguri ya rutsa da su. Dangane da ababen more rayuwa, Mista Tijjani ya ce gwamnatin ta gina tituna a cikin garin Monguno, Waka-Biu da Maiduguri, yayin da a karkashin tsaro aka samar da motocin sintiri 50 da babura 300 domin samar da kayan tsaro. “A gameda sufuri, akwai  motoci guda 30, da bas guda 25 da aka ware wa ma’aikatan gwamnati. Akwai kuma sayan kekunan lantarki guda 3,000. A kan harkar noma, akwai sayan garma da harrow guda 471 ga tararaktoci 312 da aka ware wa gamayyar kungiyoyin manoma a fadin unguwanni 312 da ke kananan hukumominmu 27. Sanarwar ta kara da cewa, “akwai kuma rabon tirela 100 na takin zamani ga manoma a fadin jihar, da kuma raba abincin dabbobi ga manoma 300 a kananan hukumomin Jere, Konduga da Mobbar.” A fannin bayar da agajin jin kai, ya ce an bayar da tallafin jin kai ga gidaje 120,000 a fadin Gwoza, Maiduguri, Jere, Kukawa, Mafa, Bama da Damboa, yayin da aka bai wa ‘yan gudun hijira 500 gidaje a Molai 500 gidaje. “Ha walau akwai niyyan cigaba da wasu ayyauka a jihar Borno da Gwamna zullum ke da muradin yi domin inganta rayuwar al'ummarsa.
0
READ ALSO
Tinubu Zai Yi Magana A Taron Kolin Yanayi Na Afirka
BY Hauwa Aliyu Balasa December 30, 2023 0

Ana sa ran shugaba Bola Tinubu zai yi jawabi a yau, 5 ga Satumba, da karfe 11 na safe, yayin cikakke...

READ ALSO
Taimakon Shugaba Tinubu Wajen Nasarar Aiki Shine Burina –Yahaya Bello
BY Hauwa Aliyu Balasa September 23, 2023 0

Gwamnan jihar Kogi Yahaya Bello, a ranar asabar ya bayyana cewa ba shi da wani buri a siyasance a ya...

READ ALSO
An Gurfanar Da Wasu Matasa A Kotu Bisa Zargin Tada Zaune Tsaye A Unguwar Wike
BY Hauwa Aliyu Balasa September 22, 2023 0

A ranar Juma’a ne rundunar ‘yan sanda ta gurfanar da wasu matasa uku a gaban wata kotun da ke Lugbe,...

READ ALSO
Gwamnatin Jihar Kwara Ta Sa Himma Wajen Bunkasa Ilimi Cikin Gaggawa
BY Hauwa Aliyu Balasa September 21, 2023 0

A cewar Gwamnan jihar Kwara, Abdulrahman Abdulrazaq samar da ingantaccen ilimi ga miliyoyin yaran da...

READ ALSO
Gwamnan Kano Ya Yi Watsi Da Hukuncin Kotu Ya Garzaya Kotun Daukaka Kara
BY Hauwa Aliyu Balasa September 20, 2023 0

Gwamnan jihar Kano, Abba Kabir Yusuf, ya ki amincewa da hukuncin kotun sauraron kararrakin zaben gwa...

READ ALSO
Saudiyya Ta Ware Wa Najeriya Gurbi 95,000-Hajjin Bana
BY Hauwa Aliyu Balasa September 20, 2023 0

Ma’aikatar Hajji da Umrah ta Saudiyya, a ranar Talata ta ware wa Najeriya gurabe 95,000 don gudanar...

READ ALSO
An Hana Yan Jarida Daukan Hukuncin Zaman Kotun Karar Apc
BY Hauwa Aliyu Balasa September 20, 2023 0

A ranar Laraba ne aka hana ‘yan jarida shiga harabar kotun da kotun sauraron kararrakin zaben gwamna...

READ ALSO
Argungu Gagarumar Bikin Al'adu Na Kamun Kifi
BY Hauwa Aliyu Balasa September 19, 2023 0

Bikin argungu wata hanya ce ta rayuwa ga al’ummar jihar Kebbi. Bikin yana kiyaye al'ada kuma yana i...

OUR CHANNELS:

SERAP Raises Alarm Over Public Officials' Lack of Accountability
BY Abiodun Saheed Omodara August 3, 2025 0

The Socio-Economic Rights and Accountability Project (SERAP) expressed its concerns on Saturday rega...


Tinubu Calls for Enhanced Regional Integration to Boost West Africa's Economic Competitiveness
BY Abiodun Saheed Omodara August 4, 2025 0

President Bola Tinubu has highlighted the crucial need for enhanced regional integration throughout...


Amnesty International Condemns Closure of Badeggi 90.1 FM as Threat to Press Freedom
BY Abiodun Saheed Omodara August 3, 2025 0

Amnesty International has condemned the shutdown of Badeggi 90.1 FM in Minna, calling the move by Ni...


165 Lives Lost and 119,791 Affected by flood Across 19 States - NEMA
BY Abiodun Saheed Omodara August 4, 2025 0

The National Emergency Management Agency (NEMA) reported that at least 165 people have died, 82 are...


Tottenham Hotspur Faces Captaincy Void as Son Heung-min Announces Exit
BY Abiodun Saheed Omodara August 3, 2025 0

Tottenham Hotspur, the reigning champions of the UEFA Europa League, will be missing their South Kor...


Team Nigeria Shines at Inaugural African School Games as Osaretin Grace Clinches Gold in Cycling
BY Abiodun Saheed Omodara August 4, 2025 0

Team Nigeria continues to assert its dominance on the continental stage, delivering a sterling perfo...


Tinubu Calls on Youth to Harness Digital Media for National Unity and Economic Growth
BY Abiodun Saheed Omodara August 4, 2025 0

President Bola Ahmed Tinubu has urged young Nigerians in the digital media sector to utilize their p...


Nigeria Immigration Service Urges Compliance with U.S. Visa Regulations
BY Abiodun Saheed Omodara August 3, 2025 0

The Nigeria Immigration Service has issued a notice urging Nigerians to utilize their U.S. visas app...


Security Guard Confesses to Gruesome Murders of School Nurse and Toddler
BY Abiodun Saheed Omodara August 3, 2025 0

A man named David Moses has admitted to the horrific murders of a school nurse and a 14-month-old ch...


Nurses Refute suspending strike, NEC to decide Saturday
BY Abiodun Saheed Omodara August 2, 2025 0

The National Association of Nigerian Nurses and Midwives and the Federal Health Institutions Sector...


More Articles

Load more...

Menu