Would you like to receive notifications on latest updates of the following headlines?

Argungu Gagarumar Bikin Al'adu Na Kamun Kifi

POSTED ON September 19, 2023 •   Hausa      BY Hauwa Aliyu Balasa

Bikin argungu wata hanya ce ta rayuwa ga al’ummar jihar Kebbi. Bikin yana kiyaye al'ada kuma yana inganta rayuwar su,ana gudanar da shi shekara-shekara kuma akan yi sa ne a watan Fabrairu kuma yana nuna ƙarshen lokacin noma da kuma lokacin kamun kifi.

Bikin ya samo asali ne da farko bisa tsarin ibada kafun aka samu sauye-sauye da gyare-gyare da dama a bikin Argungu, wanda shi ne a yau ya sa bikin ya kasance mai salo da kuma ci gaba.

Shi wannan bikin kamun kifi na Argungu yana daya daga cikin manya-manyan bukukuwan da ake gudanarwa duk shekara domin kawo karshen kiyayyar da aka kwashe tarun shekaru ana yi tsakanin yankin khalifancin Sokoto da masarautar Kebbi dake arewacin Najeriya.

[caption id="attachment_10919" align="aligncenter" width="360"] Argungu bikin kamun kifi na al'adu[/caption] Bikin Argungu ya samo asali ne a shekara ta 1934 a garin Argungu na jihar Kebbi. Shi wannan buki na kamun kifi a Argungu ya kan dauki kwana 4 ne a duk shekara kuma akan gudanar dashi ne a jihar Kebbi dake Najeriya.

Abun ban sha'awar shi ne akan kwashi kwanaki hudu ana wannan taron na al'ada,haka kuma an fi yin bikin a cikin watan Fabrairu bayan kammala duk ayyukan noma a jihar.

Akan samu sama da masunta 30,000 da suke halartar wannan bikin kamun kifi na Argungu duk shekara shekara. 

Babban dalilin taron bikin shi ne gasar kamun kifi da ake yi a kogin Mata Fada, inda ake amfani da gidan kamun kifi na gargajiya da aka kira shi da kwarya.

  [caption id="attachment_10918" align="aligncenter" width="359"] Kwaryar kamun kifi a bikin Argungu[/caption] Kafin a fara bikin kamun kifin mai kula da kogin wato sarkin ruwa kenan , zai tabbatar da cewa kogin ya samu amincewa ta hanyar sadaukarwa ga bakin kogin domin samun izininsa.

Hakan zai tabbatar da cewa kogin ba shi da tashin hankali koh fushi wajen kamun kifin, sa’anan ya kori kada da ke cikin kogin tare da gayyatar duk kifin da ke cikin kogin da ke da alaka da kogin Mata Fada. In da za a gudanar da bukin na argungu kenan .

Wani abun ban Sha’awa shi ne idan ba da izinin sarkin ruwa ba, ba za a iya kama kifi ba, domin Sarkin Ruwa shi ne mai kula da kogin Mata Fada .

Sai kuma baya ga nan duk Mai kamun kifi da ya kama kifi mafi girma zai samu kyautar da aka shirya bayarwa a shekaran,wato idan ya yi nasarar kama kifi mai nauyi sai a dora bisa sikeli.

  [caption id="attachment_10920" align="aligncenter" width="361"] Bikin kamun kifi na Argungu[/caption] Bikin kamun kifi na argungu ya zama taron kasa da kasa inda al'ummar Afirka da Turai da Amurka da sauran nahiyoyin duniya ke haduwa a tsohon garin Argungu domin halartar bikin duk shekara.

Gwamnatin jihar Kebbi ita ta dauki nauyin bikin saboda yadda ake samun farin jini da karfin tattalin arziki a jihar ta sanadiyar wannan bikin gargajiya na Argungu.

Janar Yakubu Gowon, tare da Alhaji Diori Hammani na jamhuriyar Nijar, su ne shugabanni na farko da suka halarci bikin Argungu a shekarar 1970.

Tun daga nan ne dukkan shugabannin Tarayyar Najeriya suka fara ziyartar bikin. Gwamnonin jihohi daban-daban na kasar nan musamman gwamnonin jihohin arewa su ma su kan yi marhaban don halartar wannan taron.

Rashin zaman lafiya da karuwar matsalar ‘yan fashi da tayar da kayar baya a shekarar 2009 yasa aka dakatar da wannan biki na wani lokaci amma an sake dawo da ita a shekarar 2020 domin abubuwa sun lafa.

 Bikin Argungu a halin yanzu yana daya daga cikin bukukuwan da suka shahara a Najeriya banda ma arewacin Najeriya kade harda kasashen ketere ma bikin na jan hankalin su da masu yawon bude ido a duk fadin duniya suna zuwa domin bawa idonsu abinci.

0
READ ALSO
Tinubu Zai Yi Magana A Taron Kolin Yanayi Na Afirka
BY Hauwa Aliyu Balasa December 30, 2023 0

Ana sa ran shugaba Bola Tinubu zai yi jawabi a yau, 5 ga Satumba, da karfe 11 na safe, yayin cikakke...

READ ALSO
Taimakon Shugaba Tinubu Wajen Nasarar Aiki Shine Burina –Yahaya Bello
BY Hauwa Aliyu Balasa September 23, 2023 0

Gwamnan jihar Kogi Yahaya Bello, a ranar asabar ya bayyana cewa ba shi da wani buri a siyasance a ya...

READ ALSO
An Gurfanar Da Wasu Matasa A Kotu Bisa Zargin Tada Zaune Tsaye A Unguwar Wike
BY Hauwa Aliyu Balasa September 22, 2023 0

A ranar Juma’a ne rundunar ‘yan sanda ta gurfanar da wasu matasa uku a gaban wata kotun da ke Lugbe,...

READ ALSO
Gwamnatin Jihar Kwara Ta Sa Himma Wajen Bunkasa Ilimi Cikin Gaggawa
BY Hauwa Aliyu Balasa September 21, 2023 0

A cewar Gwamnan jihar Kwara, Abdulrahman Abdulrazaq samar da ingantaccen ilimi ga miliyoyin yaran da...

READ ALSO
Gwamnan Kano Ya Yi Watsi Da Hukuncin Kotu Ya Garzaya Kotun Daukaka Kara
BY Hauwa Aliyu Balasa September 20, 2023 0

Gwamnan jihar Kano, Abba Kabir Yusuf, ya ki amincewa da hukuncin kotun sauraron kararrakin zaben gwa...

READ ALSO
Saudiyya Ta Ware Wa Najeriya Gurbi 95,000-Hajjin Bana
BY Hauwa Aliyu Balasa September 20, 2023 0

Ma’aikatar Hajji da Umrah ta Saudiyya, a ranar Talata ta ware wa Najeriya gurabe 95,000 don gudanar...

READ ALSO
An Hana Yan Jarida Daukan Hukuncin Zaman Kotun Karar Apc
BY Hauwa Aliyu Balasa September 20, 2023 0

A ranar Laraba ne aka hana ‘yan jarida shiga harabar kotun da kotun sauraron kararrakin zaben gwamna...

READ ALSO
Argungu Gagarumar Bikin Al'adu Na Kamun Kifi
BY Hauwa Aliyu Balasa September 19, 2023 0

Bikin argungu wata hanya ce ta rayuwa ga al’ummar jihar Kebbi. Bikin yana kiyaye al'ada kuma yana i...

OUR CHANNELS:

FG aims to upgrade 2,701 PHC to enhance healthcare access across Nigeria
BY Abiodun Saheed Omodara April 23, 2025 0

The Federal Government, via the National Primary Health Care Development Agency (NPHCDA), has reveal...


Education minister urges colleges to embrace dual degree system
BY Abiodun Saheed Omodara April 23, 2025 0

ABUJA, Nigeria (NAN) - The Minister of Education, Dr. Tunji Alausa, has called on stakeholders in Co...


Ginger farmers lament uncertainty ahead of 2025 planting season amid seedling shortages
BY Abiodun Saheed Omodara April 23, 2025 0

ABUJA, Nigeria - Some ginger farmers in the Bwari Area Council of the Federal Capital Territory (FCT...


Ebenezer Obey refute death rumour, says 'I Am Alive and Thriving
BY Abiodun Saheed Omodara April 22, 2025 0

The iconic musician, Ebenezer Obey-Fabiyi, has rejected the rumors regarding his death, asserting th...


Tinubu returns to address escalating violence in Nigeria after Paris trip
BY Abiodun Saheed Omodara April 22, 2025 0

ABUJA, Nigeria (NAN) - President Bola Tinubu is set to convene with the service chiefs to address th...


FG announces complete closure of Ijora bridge for urgent repairs April 27
BY Abiodun Saheed Omodara April 23, 2025 0

LAGOS, Nigeria (NAN) - The Federal Government has declared a complete closure of the Ijora Bridge in...


NPSA urges politicians to prioritise security over 2027 elections as Reps delay plenary till May 6
BY Abiodun Saheed Omodara April 23, 2025 0

The Senate and House of Representatives have delayed their plenary sessions until May 6.  In t...


Trade Wars Take Center Stage at IM ,World Bank Spring Meetings
BY Abiodun Saheed Omodara April 22, 2025 0

Global finance leaders are convening in Washington this week for the semi-annual meetings of the Int...


West Brom Terminates Mowbray's Contract after Three Months
BY Abiodun Saheed Omodara April 22, 2025 0

West Bromwich Albion, a team in the English Championship, has terminated the employment of head coac...


Leeds United's 6-0 Victory Seals Promotion alongside Burnley’s Key Win
BY Abiodun Saheed Omodara April 22, 2025 0

Leeds United and Burnley clinched promotion to the Premier League after securing the highest points...


More Articles

Load more...

Menu